Surah Az-Zalzalah in Hausa

    الزلزلة

    Surah Az-Zalzalah in Hausa

    Read Surah Az-Zalzalah in Hausa (الزلزلة) with Arabic text, Hausa translation, and audio recitation. Chapter 99 of the Holy Quran, 8 verses — free online.

    Quran in Hausa · all 114 Surahs

    1

    إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

    Idan aka girgiza ƙasa, girgizawarta.

    2

    وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا

    Kuma ƙasa ta fitar da kayanta, masu nauyi.

    3

    وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا

    Kuma mutum ya ce "Mẽ neya same ta?"

    4

    يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا

    A rãnar nan, zã ta faɗi lãbãrinta.

    5

    بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا

    cewa Ubangijinka Ya yi umurni zuwa gare ta.

    6

    يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ

    A rãnar nan mutane za su fito dabam-dabam domin a nuna musu ayyukansu.

    7

    فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ

    To, wanda ya aikata (wani aiki) gwargwadon nauyin zarra, na alheri, zai gan shi.

    8

    وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ

    Kuma wanda ya aikata gwargwadon nauyin zarra na sharri, zai gan shi.

    Az-Zalzalah

    Play